Sheikh Abduljabbar na so a mayar da shi gidan yarin Kurmawa na Kano

 


Fitaccen malamin addini, Sheikh Abduljabbar Kabara ya buƙaci hukumomi da mahukunta da su gaggauta mayar da shi gidan yarin Kurmawa da ke Kano daga gidan yarin Kuje na Abuja, inda aka kai shi bayan an sauya masa wuri da ya ce an yi masa ba bisa ƙa’ida ba.

A cikin wata wasiƙa da ya aike wa mahukunta a ranar 01 ga Janairu, 2026, Abduljabbar Kabara ya bayyana cewa watanni uku ke nan da aka sauya masa kurkuku kuma a lokacin sauyin, an hana shi ɗaukar dukkan muhimman takardun shari’arsa, waɗanda ya ce har yanzu suna Gidan Yarin Kurmawa.

Ya ce "Rashin kasancewar takardun shari’ata a hannu na haifar min da damuwa, ganin cewa ban san yanayin halin da waɗannan takardun nawa suke ciki ba a halin yanzu, alhali doka ta tanadi cewa na kasance ina da damar kula da irin waɗannan takardu da kai na.

Saboda haka, "Ni Abduljabbar Kabara ina kira ga hukumar gidan kurkukun Najeriya da sauran hukumomin da abin ya shafa da su yi gaggawar maida ni daga ina aka ɗakko ni wato kurkukun Kurmawa kenan domin na samu damar duba takardun shari’a ta tare da tabbatar da lafiyarsu da kuma kasancewarsu ƙarƙashin kulawata." in ji shi.

Post a Comment

Previous Post Next Post