Ma’aikatan jinya a jihar Kaduna sun yi barazanar tafiya yajin aiki a shekarar 2026 saboda rashin samun ƙarin girma da suka zargi hukumomin lafiya da yi
Wannan yajin aikin na iya kawo cikas ga ayyukan kiwon lafiya a jihar idan ba a gyara ba.
Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma na Najeriya (NANNM) ta jihar, kwamared Ishaku Yakubu ya bayyana rashin jin daɗinsa kan yadda ake watsi da ci gaban ma’aikatan jinya.
Ya ce, “Mun fuskanci matsaloli da dama, ciki har da rashin gudanar da tsarin ƙarin girma a ma’aikatar lafiya da wasu hukumominta,” inda ya bayyana cewa hakan yana rage ƙwarin gwiwa da aiki tukuru.
Ya ƙara da cewa ƙungiyar ba za ta ci gaba da jure jinkirin da ke cutar da ci gaban sana’a da darajar ma’aikatan jinya ba.

Post a Comment