Kotun tarayya da ke Abuja ta amince da bai wa kwamishinan kudi na jihar Bauchi, Yakubu Adamu beli a kan takardar lamuni na naira miliyan 500 da kuma sharaɗin sai ya kawo mutum biyu da za su tsaye masa.
Alkalin kotun, Justice Emeka Nwite, ya umurci cewa mutanen da za su tsaya masa su kasance suna da fili a yankunan Maitama da Asokoro ko Gwarimpa da ke Abuja, inda za a tabbatar da takardun kadarorin a wajen magatakarda.
Haka zalika, mutanen biyu za su shaida wa kotu halin arzikinsu.
Kotun ta kuma ce kwamishinan kuɗin da waɗanda za su tsaya masa za su miƙa fasfo ɗinsu ga magatakardan kotun kuma ba za su iya fita daga ƙasar ba sai da izinin kotu, sannan kuma za su miƙa hoton fasfo biyu ga kotun.
Alƙalin kotun wanda ya bayar da umarnin a riƙe kwamishinan a gidan yarin Kuje da ke Abuja har sai an cika sharuɗɗan belinsa ya ɗage shari’ar zuwa ranar 20 ga Janairu, 2026.
EFCC dai ta zargi kwamishinan kuɗin da halasta kuɗaɗen haram har na wajen dala miliyan 9.7.

Post a Comment