Rahotanni sun bayyana cewa Central Intelligence Agency (CIA) na shirin ba wa ‘yan bindigar Kurdawa makamai domin tayar da rikicin cikin gida a Iran, bayan da United States ta kasa cimma burinta a yakin da ta ƙaddamar kan Iran.
Rahoton ya ce gwamnatin Shugaba Donald Trump na tattaunawa da ƙungiyoyin ‘yan adawar Iran da shugabannin mayakan Kurdawa a Iraqi Kurdistan domin ba su goyon bayan soja, kamar yadda tashar CNN ta ruwaito daga majiyoyi da ba a bayyana sunayensu ba.
A cewar rahoton, shugaban Amurka ya kuma yi magana da shugaban abin da ake kira Democratic Party of Iranian Kurdistan, Mustafa Hijri.
An ce sojojin Amurka da Isra’ila sun fara kai farmaki kan Iran a karshen mako, lamarin da Iran ta mayar da martani da harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙi zuwa sansanonin Amurka da wuraren da Isra’ila ke mamaye.
Iran ta kuma yi gargaɗin cewa za ta mayar da martani mai ƙarfi ga duk wani yunƙuri na amfani da ƙungiyoyin mayaka daga ƙasashe makwabta.
Rahoton ya nuna cewa hare-haren sojin Islamic Revolutionary Guard Corps sun kuma yi niyya kan sansanonin ‘yan bindigar Kurdawa da jiragen sama marasa matuƙi.
Wasu tsoffin jami’an Amurka sun bayyana damuwa cewa ba a yi cikakken nazari kan sakamakon ba idan aka ba wa ƙungiyoyin mayaka makamai, saboda hakan na iya dagula tsaron yankin tare da ƙarfafa mayaka marasa kulawa.
Rahoton ya kuma ce sojojin Israel na ci gaba da kai farmaki kan wuraren sojin Iran da ke kusa da iyakar Iraq domin sauƙaƙa shigar mayakan Kurdawa arewa maso yammacin Iran.
CIA dai tana da tarihin dogon lokaci na aiki da wasu ƙungiyoyin Kurdawa a Iraki tun lokacin yaƙin Iraki, kuma tana da sansani kusa da iyakar Iran a yankin Kurdistan na Iraki, inda Amurka ke da ofishin jakadanci a birnin Erbil.

Post a Comment