Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta ɗage zaman sauraron buƙatar beli da tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami ya gabatar a kan zargin halasta kuɗin haram har zuwa ranar Laraba 7 ga wannan wata.
Tun ranar 31 ga watan Disamba, kotu ta tasa ƙeyar Abubakar malami zuwa gidan yarin Kuje.
EFCC dai ta tuhumi tsohon ministan shari’ar ne da ɗansa Abdul‘aziz da kuma mai ɗakinsa Asabe Bashir kan halasta kuɗin haram har na naira biliyan 8.7, zargin da dukkansu suka musanta.
Hakan dai na nufin Abubakar Malami zai ci gaba da zama a gidan yarin na Kuje har zuwa tsakiyar makon gobe.
.jpeg)
Post a Comment