An ji ƙarar hare-harbe a gangamin goyon bayan Wike a Bayelsa



An samu hatsaniya bayan da aka ji ƙarar harbe-harbe a wurin gangamin goyon bayan Ministan Abuja,Nyesom Wike da aka gudanar a Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa.

Kafofin yaɗa labaran Najeriya sun ce gangamin wanda ƙungiyar NEW Associates mai goyon bayan wike ta shirya an gudanar da shi ranar Asabar.

Ana tsaka da gangamin en lkacin da aka riƙa jin ƙarar harbe-harbe a kusa da inda ake gangamin. Daga baya an maido da zaman lafiya.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai, Sakataren ƙungiyar NEW Associates a jihar Bayelsa, Comrade Ebilade Ekerefe, ya ce babu wabin da zai hana ci gaba da gangamin.

Post a Comment

Previous Post Next Post