Uromi: Gwamnan jihar Edo ya dakatar da ayyukan ƴan sa-kai

 

Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo ya dakatar da ayyukan ƴan sa-kai da aka fi sani da vigilante a faɗin jihar baki ɗaya.

Haka kuma gwamnan ya dakatar da kwamandan askarawan tsaron jihar, Friday Ibadin.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Umar Musa Ikhilor ya fitar, inda ya ce gwamnan ya ɗauki wannan matakin ne bayan samun rahoton farko-farko na kisan matafiya ƴan arewa a yankin Uromi da ke jihar.

Ya ce "ƴan sa-kan da suka kashe matafiya a ranar 27 ga watan Maris ba su da rajista da hukumar askarawan tsaron jihar Edo. Aika-aikar da suka yi ba al'adar mutanen Edo ba ce, kuma gwamnatin Okpebholo ba za ta aminta ba.

"Ana cigaba da gudanar da bincike, kuma tuni an kama mutum 14, sanna ana farautar sauran," kamar yadda sanarwar, wadda tashar Channels ta ruwaito ta nuna.

Post a Comment

Previous Post Next Post