Dr. Zarif Ya Isa Iraƙi Bayan Wata Gayyata Da Ya Samu

Mr. Muhammad Javad Zarif, mataimakin shugaban kasar Iran kan harkokin dabaru, ya isa birnin Bagadaza ne sa'o'i kadan da suka gabata, bisa gayyatar Mr. Ammar al-Hakim, shugaban kungiyar Hikima ta kasar Iraki, domin halartar taron kasa da kasa karo na uku mai taken "Hakkin makomar Mabiya Ahlul Baiti (amincin Allah a gare shi)".


 Bayan isowarsa, Zarif ya ziyarci wurin tunawa da Kwamandojin Nasara, inda ya kai gaisuwa ga ruhin shahidi Qassem Soleimani da shahidi Abu Mahdi Al-Muhandis. 

 Sannan ya je hedikwatar kungiyar Hikima ta kasa don ganawa da Malam Ammar Al-Hakim da tattaunawa da shi.

Post a Comment

Previous Post Next Post