An Gudanar Da Addu'ar Bakwai Na Kareema Sambo


Daga Mardiyya Kabiru

A ranar Litinin 20/01/2025 ‘yan'uwa musulmi almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) dake Garin Bomo, suka gudanar da addu'ar bakwai na Kareema Sambo a muhallin Fudiyyah Bomo.

Bayan saukan karatun Alkur'ani mai girma da aka gudanar an kara da mashahuran addu’o’i duk hadiya zuwa ga Marigayiya Khareemat. Daga nan aka karanta addu'ar  ziyarar Imam Hussain (A.S) sai Du’a Tawassul.

Allah ya jibanci Marigayiyah Khareemat ya sada ta da masoyanta A’immatu Ahlul baiti (AS).

-MEDIA FORUM BOMO





Post a Comment

Previous Post Next Post